/> Jami’an tsaron Saudiyya sun kama mutumin da ya zagi matar MANZON ALLAH SAW - Arewa24
Lorem ipsum dolor sit amet, consectetur adipiscing elit. Test link
AGCYSWP78
Posts

Jami’an tsaron Saudiyya sun kama mutumin da ya zagi matar MANZON ALLAH SAW


 Jaridar Labaran Hausa ta ruwaito cewa.


Rundunar ‘yan sanda a birnin Riyadh ta tabbatar da kama wani mutumi wanda ya zagi Sayyada Aisha R.A, matar Annabi Muhammad (SAW).

Manjo Khaled Al-kraidis, wanda yanke shine kakakin rundunar ‘yan sandan Riyadh, ya bayyana cewa a wani bidiyo da aka wallafa a shafukan sadarwa, an gano cewa bidiyon cin mutuncin ne ga Annabi Muhammad (SAW), haka kuma zagi ne ga uwar muminai, Aisha (R.A).

Bayan kama mutumin an gabatar dashi a gaban kotu domin yanke masa hukumcin daya dace da shi.

An wallafa bidiyon ne a shafukan sadarwa a ranar 10 ga watan Muharram, a lokacin da ‘yan kungiyar Shia suke nuna bakin cikinsu kan kisan da aka yiwa Sayyadina Hussain a lokacin yakin Karbala.

A Musulunci, duka matan Annabi Muhammad guda 11 ana daukar su a matsayin iyaye a Musulunci, a ka’ida ma Musulmai suna so da kuma girmama su fiye da iyayen da suka haife su. 
L